An Kashe Fursunoni 129 da su kai Yunƙurin Tserewa a DR Congo

 

Ministan cikin gida na Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo, Jacquemain Shabani Lukoo, ya bayar da rahoton cewa, fursunoni 129 ne aka kashe a wani yunƙurin tserewa daga gidan yarin Makala da ke Kinshasa, wanda shi ne gidan yari mafi girma kuma mafi suna a ƙasar.

Daga cikin waɗanda suka mutu, an harbe 24, yayin da wasu suka mutu sakamakon shaƙe musu wuya da aka yi da kuma turmutsutsu.

Lamarin ya kuma yi sanadin raunata mutum 59 a gefe guda kuma an yi wa mata da yawa fyaɗe.

Gobara ta kuma lalata wasu muhimman cibiyoyin gidan yarin da suka haɗa da gine-ginen gudanarwa da ma’ajiyar abinci.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama sun kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kan zargin kisan gilla da aka yi a lokacin tserewa daga gidan yarin.

Ƙungiyoyin sun yi amannar cewa cunkoson fursunoni 14,000 a gidan yarin wanda aka gina da zai iya ɗaukar fursunoni 1,500 kaɗai ne ya haddasa tarzomar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here