Adadin Mutanen da Aka Kashe a Zanga-Zangar Bangladesh

 

Masu zanga zanga a Bangladesh na kira ga Firaimistan kasar Sheikh Hasina ta sauka daga mukaminta, yayin da dubban masu zanga zangar suka hallara don maci zuwa Dhaka.

Halin da ake ciki a babban bbirnin kasar ba dadi domin ana cikin zaman dar-dar.

Gwamnatin kasar ta sanar da hutun kwanaki uku inda aka rufe dukkan harkokin kasuwanci da kuma kotuna.

An toshe hanyar shiga Dhaka, inda aka tsaurara matakan tsaro a sassan birnin, sannan an sake dauke intanet a wasu sassan na kasar.

A jiya Lahadi an kashe mutum fiye da casa’in a gwabzawar da aka yi da jami’an tsaro ciki har da jami’an ‘yan sanda da dama.

A watan da ya gabata ne aka fara bore saboda sabon tsarin da gwamnati ta fito dashi na rabon guraben aiki abin da bai wa ‘yan kasar musamman dalibai dadi ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here