Gwamnatin Kebbi ta Sanya Hannu Kan Dokar Mafi ƙarancin Albashin N75,000

 

Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris ya sanya hannu a kan sabuwar dokar tsarin albashi mafi ƙanƙanta – naira 75,000, ga ma’aikatan jihar.

A lokacin bikin sanya hannu a kan dokar, da aka yi yau Laraba a fadar gwamnatin jihar da ke Birnin Kebbi, gwamnan yaa jaddada ƙudurinsa da kare muradun ma’aikata da kuma tabbatar da jin daɗinsu.

Ya yi alƙawarin cewa ba zai taɓa barin ma’aikatan jihar su kunyata ba, inda ya ce sun kafa tarihi, kasancewar ya sanya hannu a kan dokar ne a ranar da majalisar gudanarwar ƙungiyar ƙwadago ta ƙasar ta NLC ke gudanar da taronta a jihar, inda shugaban ƙungiyar Joe Ajaero ya kasance a wurin.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Gwamnan ya taka muhimmiyar rawa wajen batun aiwatar da sabon tsarin albashin mafi ƙanƙanta a Najeriya.

Ta ce a lokacin da yawancin gwamnoni ke cewa ba za su iya biyan sabon albashin ba, shi kuwa ya yi tsayin daka kan cewa gwamnoni za su iya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here