Kwamishinan ‘Yan Sanda a Raba wa Masu Zanga-Zanga Ruwa da Biskit a Jihar Edo

 

 

Kwamishinan ‘yansanda na Edo ya faɗa wa masu zanga-zanga a jihar cewa shi “abokinsu” ne kuma sun je inda suke ne domin su ba su kariya.

Da yake yi wa masu zanga-zangar jawabi a birnin Benin, CP Funsho Adegboye ya ce sun zo wa masu zanga-zangar da ruwa da kuma ɗan abin taɓawa.

“Da ma na sha yin kira a gare ku da mu mazauna jihar Edo mu kafa misali a zanga-zangar lumana, kuma abin da na gani zuwa yanzu sai dai kawai na gode muku,” a cewarsa.

“Ina roƙonku mu cigaba a haka ta yadda sauran jihohi za su yi koyi da mu a zanga-zangar lumana…Za mu ba ku ruwa, da biskit da sauran abin taɓawa.”

Jihar Edo na ɗaya daga cikin jihohin da zanga-zangarsu ba ta yi muni ba a faɗin Najeriya, yayin da ‘yanƙasar ke nuna fushinsu game da tsadar rayuwa da rashin shugabanci nagari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here