Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya ta yi Kira ga Likitoci Akan Suyi Hakuri su Koma Teburin sulhu

 

Yau Kwana na biyu da Likitoci a Najeriya suka sake shiga yajin aiki.

Likitocin sun zargi gwamnatin tarayya da rashin cika alkawuranta.

Gwamnatin tarayya na kira da Likitocin suyi hakuri su koma teburin sulhu

Abuja – Karamin Ministan Lafiya, Dr. Olorunimbe Mamora, a ranar Talata, ya yi kira ga shugabannin kungiyar Likitoci masu neman kwarewa NARD su koma teburin sulhu.

Gwamnati tace tana iyakan kokarinta wajen canza tunanin da ake mata a bangaren lafiya. Mamora ya bayyana hakan ne a taron kungiyar likitoci NMA, shiryar birnin tarayya, rahoton Punch.

Tace:

“Gwamnati na kokarin kawo gyara. Ba zai yiwu muyi kasa a gwiwa ba. Ina amfani da wannan dama in yi kira ga Likitocin dake yajin aiki yanzu su dawo teburin sulhu saboda a tattauna dukkan matsalolin.”

“Wannan shine roko na. Ko a faggen yaki, abokan adawa a karshe na komawa teburin sulhu domin tattauna matsaloli.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here