Rundunar Sojojin Najeriya ta yi Martani Kan Batun Cewa Tana Shirin Sakin ‘Yan Boko Haram

 

An yi watsi da rahotannin cewa rundunar sojojin Najeriya na niyan sakin akalla ‘yan ta’addan.

Boko Haram biyu da ke hannunta Mai magana da yawun NA, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu ne ya yi wannan raddi, a ranar Talata, 10 ga watan Agusta.

Nwachukwu ya yi bayanin cewa rundunar, ta hanyar Operation Safe Corridor, na shirin gyara maharan tare da tura su ga hukumomin da suka dace daga bisani.

Rundunar Sojojin Najeriya ta mayar da martani game da ikirarin karya da ke cewa tana shirin sakin wasu kwararrun yan Boko Haram guda biyu wadanda a halin yanzu ake yi masu gyara.

A cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafinta na Facebook, mai magana da yawun NA, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu, ya lura cewa mutanen da ke yada irin wannan karairayi suna yi ne da gangan don cimma munanan manufofi.

A wani yunƙuri na daidaita gaskiyar lamari, Nwachukwu ya ce a matsayinsu na ƙwararrun hukuma, rundunar ta yanke shawarar cewa “za a karɓi duk ‘yan ta’adda da suka mika wuya, a sarrafa su, sannan a mika su ga hukumomin da suka dace na gwamnati don ci gaba da kulawa daidai da manyan tanade -tanade.”

Ya yi bayanin cewa Operation Safe Corridor da ke gudana, wanda ke kula da aikin gyaran, hukuma ce da gwamnatin tarayya ta kafa ba NA ba kuma don haka, kuskure ne a yanke cewa rundunar za ta ‘yantar da ‘yan ta’addan da suka tuba.

Kakakin ya bayyana cewa Sojojin Najeriya ba za su taba yin hakuri ba, karfafawa, ko shiga cikin duk wani aiki na rashin bin doka kamar kisan gilla.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here