MDD da Shugabannin ƙasashen Duniya Sun yi Allah Wadai da Hare-Haren Isra’ila a Gaza

 

Shugabannin ƙasashen duniya sun fara tofa albarkacin bakinsu kan hare-haren baya-bayan nan da Isra’ila ta kai a Gaza da suka yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 400.

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya ce ya ‘kaɗu’ da hare-haren, kuma ya yi kira da babbar murya da a mutunta yarjejeniyar tsagaita wutar.

Firaminstan Australia Penny Wong ya ce ƙasarsa na buƙatar ɓangarorin biyu su mutunta tsagaita wutar, inda ya ce ”wajibi ne a kare dukkanin fararen hula”.

Shi kuwa mataimakin Firaministan Belgium, Maxime Prevot, ya yi alawadai ne da hare-haren, inda ya yi kira ga duka ɓangarorin su tsaya kan yarjejeniyar, domin” kar a koma gidan jiya”.

Mai magana da yawun gwamnatin Rasha Dmitry Peskov shi ma ya bayyana lamarin a matsayin abin damunwa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here