MDD ta yi kira ga Sojojin Sudan da su Gaggauta Sakin Waɗanda aka Kama ba Bisa Ka’ida

 

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi kira ga sojojin Sudan su “gaggauta sakin waɗanda aka kama ba bisa ka’ida ba ko kuma aka yi masu ɗaurin talala.

Firaminista Abdallah Hamdok yana cikin shugaban farar hula da rahotanni suka ce wasu sojoji sun yi wa ɗaurin talala a ranar Litinin.

Manzo na musamman a Sudan Volker Perthes ya ce “na damu sosai game da rahotannin juyin mulki da kuma yunƙurin yin zagon ƙasa ga dawowa tafarkin dimokuradiyya a Sudan.Rahotannin kama Firaminista da jami’an gwamnati da ƴan siyasa ba abin amincewa ba ne.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here