Ambaliyar Ruwa: Mutane 11 Sun Mutu a Jihar Neja

 

Mummunar ambaliya ruwa ta yi sanadin mutuwar mutum 11 a jihar Neja da ke tsakiyar Najeriya, tare da lalata garuruwa masu yawa faɗin ƙananan hukumomi 19 daga cikin 25 da ke jihar.

Cikin wata sanarwa da daraktan hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar, Abdullahi Baba-Arah, ya fitar ya ce lamarin ya lalata gidaje fiye da 6,865, tare da gonaki 118,692, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

Lamarin ya jefa fiye da mutum 41,000 cikin tsananin buƙatar tallafi.

Baya ga lalata gonakin, ambaliyar ta kuma shafi makarantu 246, lamarin da ya shafi harkokin ilimi a garuruwa 529 na jihar.

Ƙananan hukumomin da lamarin ya fi ƙamari sun haɗa da Mokwa da Katcha da Lavun da Lapai da Agaie da Shiroro da Munya da Gbako da Kontagora da Bosso da Edati da Agwara da Bida da Magama da Mashegu da Borgu da Gurara da Suleja da ƙaramar hukumar Rijau.

Rahotonni sun ce ambaliyar ta kuma shafi gadoji 18 da kwalbatoci 80, lamarin da ya kawo cikas ga harkokin sufuri a wasu yankunan jihar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here