Gwamnatin Najeriya ta Buƙaci ƙarin Tallafin MDD Kan Ambaliyar Maiduguri

 

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya Kashim Shettima ya gana da Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres a shalkwatarta da ke birnin New York na Amurka.

Cikin wani saƙo da kakakin Majalisar Dinkin Duniya ya wallafa a shafinsa na X, ya ce a lokacin ganawar an tattauna batutuwa da dama da suka shafi tsaro da ayyukan jin ƙai da tattalin arziki da sauransu.

Shettima wanda yake wakiltar Shugaba Bola Tinubu a babban taron Majalisar Dinkin Duniyar karo na 79 ya kuma zanta da mataimakiyar Sakatare-Janar ta majalisar, Amina Mohammed.

Mataimakin shugaban ƙasar ya kuma buƙaci ƙarin tallafi domin magance matsalolin da sauyin yanayi suke janyowa, inda ya nanata buƙatar ƙarin tallafi ga mutanen da ambaliya ta illata a jihar Borno.

A nasa ɓangaren, Mista Guterres ya jajanta wa Najeriya, sannan ya yi alƙawarin samar da ƙarin tallafin.

Ya ce Majalisar Dinkin Duniya za ta cigaba da tallafa wa Najeriya, sannan ya jinjina wa shugaba Tinubu, inda ya ce Najeriya ƙawar arziki ce ga Majalisar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here