Ƙungiyar NCYP ta Magantu Kan Yarjejeniyar da Gwamna Uba ya Cimmawa da Kamfanin China

 

Jihar Kaduna – Ƙungiyar matasan kiristocin Arewa (NCYP), ta ba gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani shawara.

Ƙungiyar NCYP ta buƙaci Gwamna Uba Sani ya guji tafka irin kura-kuran da magabacinsa Nasir El-Rufai ya yi a yayin da yake ƙulla yarjejeniya da ƙungiyoyin ƙasashen waje a madadin jihar.

An yabawa Gwamna Uba Sani

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban NCYP, Isaac Abrak, ya fitar a ranar Talata, cewar rahoton jaridar The Cable.

Shugaban NCYP ya yabawa gwamnan bisa rattaɓa hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da kamfanin Huawei na ƙasar China.

Isaac Abrak ya bayyana yarjejeniyar a matsayin wata gagarumar nasara da za ta iya inganta ɓangaren ICT na jihar da kuma samar da sababbin damammaki ga matasa.

“El-Rufai ya bar Kaduna da bashi”, NCYP

Ya yi tsokaci kan gwamnatin El-Rufai da ta karɓo lamunin $350m daga bankin duniya domin bunƙasa ilimi wanda daga ƙarshe ba a cimma manufar da ta sanya aka karɓo shi ba.

“Muna kira ga gwamnati da ta guji yin irin kura-kuran da aka yi a baya, musamman waɗanda aka yi a gwamnatin da ta shuɗe ƙarƙashin jagorancin Nasir El-Rufai da ta ci bashin $350m domin bunƙasa harkar ilmi.”

“Abin takaici ba a cimma manufar wannan bashin ba, sannan a yau an bar mutanen jihar Kaduna da nauyin biyan bashin da bai amfanar da komai ba.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here