Hukumar NDLEA ta Kama Makudan Daloli na Jabu a Abuja

 

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta NDLEA a Najeriya ta ce jami’anta sun kama makudan daloli na jabu a Abuja.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta ce an yi yunƙurin sace kusan dala biliyan 2.7 na tattalin arzikin Najeriya ta hanyar tura kuɗaɗen na jabu a kasuwa da suka kai sama da dala miliyan 4.7.

Hukumar ta ce jami’anta sun kama kuɗaɗen a yankin Abaji da aka ɗauko daga Legas zuwa Abuja.

Wannan an kama wanda ake zargi da fataucin kuɗin mai suna Abdulmumini Maikasuwa.

Hukumar ta ce shugabanta Birgediya Janar Buba Marwa ya bayar da umarnin a miƙa kuɗaɗen da wanda ake zargi ga hannun hukumar EFCC domin ci gaba da bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here