Kungiyar NCL ta yi Allah Wadai da Kama Shugabanta

 

FCT, Abuja – Kungiyar kwadago ta yi martani bayan jami’an DSS sun kama Joe Ajaero a yau Litinin.

Kungiyar NCL ta yi Allah wadai da lamarin kuma ta bukaci a gaggauta sake shugabanta, Joe Ajaero cikin gaggawa.

Legit ta tatttaro abin da kungiyar kwadago ta fada ne a cikin wani sako da NLC ta wallafa a shafinta na Facebook.

NCL: ‘Ana cin zarafin ma’aikata a Najeriya’

Kungiyar yan kwadago ta NLC ta bayyana cewa ana cigaba da cin zarafin ma’aikata a fadin Najeriya.

NCL ta fadi haka ne bayan an kama shugaban kwadago na kasa, Joe Ajaero a birnin tarayya Abuja.

NCL ta bukaci a daina cin zarafin ma’aikata

Kungiyar kwadago ta wallafa cewa dole ne a daina cin zarafin ma’ikata a Najeriya ta hanyar kama shugabannin ta.

Yan kwadago sun ce baraza da cin fuska da ake musu a Najeriya dole ne a tabbatar da cewa sun zo karshe.

Yanzu haka Joe Ajaero yana ina?

Kungiyar kwadago ta bayyana cewa yanzu haka ana rike da shugabanta, Joe Ajaero a ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro.

Haka zalika kungiyar ta ce an kama Joe Ajaero ne yayin da zai tafi taron yan kwadago a kasar Birtaniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here