Olusegun Obasanjo ya Siffanta Ahmad Joda a Matsayin ‘Dan Najeriya na Gaske Wanda ya Tabbatar da Hadin Kai da Cigaban Najeriya

 

An jinjinawa Alhaji Ahmad Joda da wasu tsaffin sakatarorin din-din-din kan hadin kan Najeriya.

A cewar Obasanjo, sun yi wannan gwagwarmaya ne lokacin juyin mulki a 1966.

Tsohon shugaban kasan ya siffanta Joda matsayin jajirtaccen dan Najeriya.

Ota, Ogun – Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo, ya bayyana yadda tsohon sakataren gwamnati, Alhaji ahmad Joda, da sauran manyan sakatarorin din-din-din suka kare Najeriya daga barkewa bayan juyin mulkin 1966.

Obasanjo, yayin aika sakon ta’aziyyarsa ta bakin mai magana da yawunsa, Kehimde Akinyemi, ya siffanta Joda a matsayin dan Najeriya na gaske wanda ya tabbatar da hadin kai da cigaban Najeriya.

A cewar Obasanjo, “Na san bai cin Joda da wasu Sakatarorin din-din-din irinsa lokacin tashin tashina a 1966, da Najeriya ta yi kaca-laca. Saboda Araba ya lashi takobin raba kasar nan.”

“Amma Ahmad Joda da sauran manyan jami’an gwamnati irinsu Philip Asiodu, Liman Ciroma, Alison Ayida ne suka tabbatar Najeriya bata balle ba.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here