Shugaba Buhari ya Nada Gwamna Okowa a Matsayin Memba a Kwamitin Kawo Sauyi na Fannin Kiwon Lafiya

 

Muhammadu Buhari ya nada gwamnan Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin memba a kwamitin kawo sauyi na fannin kiwon lafiya.

Kwamitin da shugaban kasa ya kaddamar a ranar Litinin yana da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo a matsayin shugabanta.

Wasu fitattun likitocin kiwon lafiya kamar Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, suma membobin kwamitin ne.

An nada Gwamna Ifeanyi Okowa a matsayin mamba a kwamitin kawo sauyi a fannin kiwon lafiya wanda mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ke jagoranta.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya kaddamar da kwamitin a ranar Litinin, 6 ga watan Satumba, jaridar The Cable ta rawaito.

A cewar wata sanarwa da daya daga cikin hadiman shugaba Buhari kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ya fitar, an kafa kwamitin ne don ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a bangaren.

Sauran membobin kwamitin sun hada da Osagie Ehanire, Ministan Lafiya da kuma Shugabannin Kungiyar Likitocin Najeriya (NMA), Kungiyar Magunguna ta Najeriya, kungiyar ma’aikatan jinya da kungiyar gwaje-gwaje ta Najeriya, Vanguard ta rawaito.

Gidauniyar Bill & Melinda Gates da Vesta Healthcare Partners za su yi aiki a matsayin masu sa ido a cikin kwamitin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here