Kaduna: Jam’iyyar PDP ta Lashe Zaben Karamar Hukuma a Mazabar Gwamna El-Rufa’i
Gwamna El-Rufa’i ya rasa akwatin zabensa ga jam’iyyar PDP a zaben kananan hukumomi.
Gwamnan ya kada kuri’arsa da safiyar Asabar a akwatin zaben.
A cewar El-Rufa’i, ba dole bane jam’iyyarsa ta lashe kowani zabe ba.
Kaduna – Jam’iyyar Peoples Democratic Party PDP ta lashe akwatin zabe kujerar shugaban karamar hukumar da kuma na kansila a mazabar gwamnan jahar, Nasir El-Rufa’i.
El-Rufa’i ya kada kuri’arsa da safe a akwatin mazabarsa dake Unguwar Sarki, karamar hukumar Kaduna ta Arewa, rahoton ChannelsTV.
Read Also:
Yayinda yake kada kuri’arsa, El-Rufa’i ya bayyana cewa bai zama dole jam’iyyarsa ta APC ta kashe zabe ba, kawai abinda yake bukata shine inganta zabe ta hanyar amfani da na’urar zamani.
A cewar gwamnan, kawo wannan na’urar ua nuna cewa gwamnatin APC a jahar Kaduna ba tada shirin magudin zabe.
Yayin sanar da sakamakon zaben, baturen zaben mazabar, Muhammad Sani, ya ce jam’iyyar APC ta samu kuri’u 62 a zaben shugaban karamar hukumar, yayinda PDP ta samu kuri’u 86.
A zaben Kansila kuwa, APC ta samu kuri’u 53 yayinda PDP ta samu kuri’u 100.
Yanzu haka, ana cigaba da tattara sakamakon zabe a matattarar zabe na karamar hukumar Kaduna ta kudu.