Dan takarar Gwamnan Kano karkashin jam’iyyar PDP Abba K. Yusuf ya auka cikin rudani, abinda ya sanya ya dauko hayar kwararren lauya mai mukamin SAN dan kare takararsa.

A ranar biyu ya watan Oktoba ne a wani yanayi mai cike da ayar tambaya, aka yi wani Abu da aka kira zaben fidda gwani na dan takarar Gwamnan Kano karkashin inuwar jam’iyyar PDP a Gidan Kwankwaso dake kan titin Lugard, kuma aka bayyana Abba Kabiru Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben.

Sai dai kuma, mutumin da aka bayyana cewar ya zo na biyu a wannan zaben, Jafar Sani Bello ya shiga da kara gaban Mai Shariah AT Badamasi yana rokon da kotun ta ayyana shi a matsayin dan takarar PDP sakamakon rashin cika ka’idar da Abba K. Yusuf yayi na shigowa PDP din.

A cewar Lauyan Jafar Sani Bello, ya bayyanawa kotu cewar Abba Kabiru Yusuf ya karya sashi na 8 karamin kashi na 8 da ya bayyana cewar tilas wanda duk ya yiwa jam’iyyar kome ya rubuta wasika zuwa ga Shugabancin mazabarsa domin shaida musu komarsa jam’iyyar, abinda yace Abban bai yi ba.

A saboda haka ya roki kotun da ya ayyana Jafar Sani Bello a matsayin dan takarar Gwamnan Kano karkashin inuwar jam’iyyar PDP sakamakon rashin bin doka da Abban yayi na komawa jam’iyyar.

The post PDP: Takarar Gwamnan Kano ta Abba K. Yusuf na cikin tsaka mai wuya appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here