Rikici ya Kaure a Jahar Kaduna, Mutane 30 Sun Rasa Rayukansu

 

Aƙalla mutum 30 suka mutu sannan an kona gidaje da dama a kauyukan Madamai da Abun na karamar hukumar Kaura da ke jahar Kaduna.

Jaridar Daily Trust ta rawaito tsohon shugaban kungiyar hadin-kan matasan Kaura, Kwamared Derek Christopher na cewa maharan sun kutsa yankunan da misali karfe 5 na yamma suka rinka harbe-harbe kan mai uwa dawabi.

Ya kuma shaida cewa yawancin mutanen da aka jikkata an kai su asibiti domin basu kulawa.

Rundunar ‘yan sanda Kaduna kawo yanzu ba ta ce komai a kan harin ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here