Ba Zamu Shiga Yaƙi da Iran ba, Duk da Matsin Lambar Trump – Birtaniya

 

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya ce ƙasarsa ba za ta shiga yaƙi da ƙasar Iran ba, duk da matsin lambar da yake fuskanta daga shugaban Amurka, Donald Trump.

Da yake magana a wani taron manema labarai a yau, Starmer ya bayyana cewa akwai matsin lamba mai yawa a kansa domin ya sauya matsayinsa kan shiga yaƙin, amma ya jaddada cewa ba zai canza wannan matsaya ba.

Ya ƙara da cewa a matsayinsa na Firaminista, zai ci gaba da yanke shawara ne bisa muradun ƙasar Birtaniya.

Lokacin da aka tambaye shi ko yana ƙara kusantar Turai sakamakon dangantakar da ta yi tsami da Trump, Starmer ya ce ba zai zaɓi tsakanin Amurka da Turai ba.

Ya ce, “Yana da muhimmanci a gare mu mu ci gaba da samun kyakkyawar alaƙa da Amurka da kuma Turai baki ɗaya.”

A nasa ɓangaren, Trump ya shaida wa jaridar The Telegraph cewa yana duba yiwuwar ficewar Amurka daga ƙungiyar NATO da muhimmanci.

Trump ya sha sukar NATO da kuma Birtaniya kan rashin shiga yaƙin da Amurka ke yi da Iran.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here