Shugaban Mulkin Soji a Sudan, Al-Burhan ya Tsallake Rijiya da Baya

 

Shugaban rundunar sojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya tsallake rijiya da baya a wani yunkurin kashe shi a wata ziyara da ya kai sansanin soji da ke gabashin kasar.

Janar Burhan yana halartar bikin yaye dalibai a sansanin sojojin na Gibet lokacin da wani harin da jiragen yaki mara matuki suka kai musu. Mutane 5 ne suka mutu yayin lamarin.

Wani mai magana da yawun rundunar wanda ya zanta da BBC ya zargi ‘yan tawayen Rapid Support Forces RSF da hannu a kai harin. RSF ba ta mayar da martani kan zargin ba.

Harin dai shi ne na baya bayan nan a wasu jerin hare-hare da aka kai kan sansanonin sojin da ke kusa da Port Sudan da ke gabar tekun Bahar Maliya.

Babu wanda ya dauki alhakin kai harin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here