Borno: Sojojin Najeriya Sun Kashe Wasu Daga Cikin ‘Yan Boko Haram

Dakarun rundunar Operation Fire Ball ta sojojin Najeriya sun kashe mayaƙan ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP guda 16 a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Muƙaddashin shugaban sashen yaɗa labaran rundunar, Bernard Onyeuko ne ya bayyana haka ranar Lahadi cikin wata sanarwa, yana mai cewa Operation Fire Ball wani ɓangare ne na rundunar Operation Lafiya Dole da ke yaƙi da ‘yan ta’adda.

Birgediya Janar Onyeuko ya ce dakarunsu sun lalata motar bindiga guda huɗu na ‘yan ƙungiyar tare da ƙwato akwatun harsasai yayin harin.

Ya ce a ranar 21 ga Oktoba sun kula da wasu motoci suna bin bayan jerin gwanon motocinsu da ke kan hanyar mayar da ‘yan gudun hijira garin Baga daga Maiduguri, suna ƙoƙarin shiga cikinsu.

A cewarsa, dakarun sun far musu nan take, inda suka kashe uku daga cikinsu tare da lalata motar bindiga ɗaya.

Kazalika, dakarun da ke sansanin Army Super Camp a Magumeri sun kashe mutum 11 a wata arangama da suka yi sannan suka kama wasu makaman harbo jirgi guda uku, a cewar Mista Onyeuko.

Bayan wannan fafatawar ne kuma aka kashe wasu guda biyu yayin da wasu suka tsere da munanan raunuka.

A jiya Asabar ma sai da jami’an tsaro suka kashe ‘yan Boko Haram shida a Jihar Yobe mai maƙwabtaka, yayin wani hari da ‘yan Boko Haram suka kai a garin Babban Gida. Ɗan sanda ɗaya ya rasa ransa a fafatawar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here