Sojojin Najeriya: Ba mu Kashe Kowa ba a Filato Yayin Satar Kayan Abinci

 

  Hedikwatar tsaro ta sojojin Najeriya ta musanta zargin cewa sojoji sun kashe mutum huɗu a Jihar Filato yayin da matasa ke ƙoƙarin wawashe gidan tsohon Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Yakubu Dogara.

A jiya Juma’a ne jaridar Vanguard ta ruwaito cewa dakarun rundunar Operation Safe Heaven (OPSH) sun halaka mutum huɗu tare da jefa gawarwakinsu a cikin kogi a garin Gwafan da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.

“Wannan rahoto abin cutarwa ne ga sojojin Najeriya da kuma Operation Safe Heaven, waɗanda suka tabbatar da zaman lafiya a Filato,” in ji hedikwatar tsaron cikin wata sanarwa a yau Asabar.

Sai dai sanarwar ta tabbatar cewa sojojin sun je wurin da abin ya faru kuma har ma sun kama ɓarayin guda 30.

“Saboda dalilai na tarihi, a ranar Lahadi 25 ga watan Oktoban 2020, ‘yan daba sun shiga gidan tsohon kakaki a Lamingo domin yin sata,” a cewar hedikwatar tsaron.

Ta ci gaba da cewa: “Daga baya, dakarun OPSH da ke aikin dawo da zaman lafiya a Jihar Filato da kewaye suka isa wurin domin shawo kan lamarin. Cikin ƙwarewa da bin dokokin aiki, mun kama jumillar barayi 30 a wurin.

“Bugu da ƙari, ‘yan daba 114 aka kama, mata 21 da maza 93, da laifin sata. Idan ba a manta ba sai da aka gabatar da su ga manema labarai.”

An sha zargin rundunar sojojin Najeriya da kisan masu zanga-zangar EndSars da aka kwashe mako biyu ana yi a Lekki Toll Gate da ke Jihar Legas. Sai dai sun musanta zargin, suna masu cewa ba su je wurin ba gaba ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here