Dakarun Somaliya Sun ƙwato Gini Daga Hannun Mayaƙan Al-Shabab

 

Kafofin yaɗa labaran Somaliya sun ce dakarun ƙasar sun yi wa wani ginin gwamnati a tsakiyar birnin Mogadishu ƙawanya, domin kawo ƙarshen mamayar da mayaƙan al-Shabab ta yi wa ginin.

Lamarin ya fara ne da harin bom a cikin wata ƙaramar mota a kofar shiga ginin a gundumar Hamarweyne, kafin daga bisani mayaƙan waɗanda suka ɓatar da kama a matsayin sojoji su mamaye ginin.

Ma’aikatar yaɗa labaran ƙasar ta ce jami’an tsaro sun samu nasarar kuɓutar da duka ma’aikatan da ke cikin ginin, tare da kashe mayaƙan al-Shaban shida a ƙoƙarin kwato ginin.

Kafofin yaɗa labarai masu alaƙa da ƙungiyar sun ambato mai magana da yawun ƙungiyar na cewa sun kashe ma’aikatan gwamnati 34.

A shekarar 2019 ƙungiyar al-Shabab ta kai harin ƙunar bakin wake a kan ginin tare da kashe magajin birnin na wancan lokaci Abdirahman Omar Osman.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here