Sule Lamido ya yi Martani Kan Tsige Shugaba Buhari

Alhaji Sule Lamido, tsohon gwamnan Jigawa ya ce bai dace a dinga kiraye-kirayen tsige Buhari ba.

Ya tabbatar da cewa wannan lamarin ba zai samu goyon bayan shi ba ko kadan.

Ya sanar da hakan ne a wani taron rantsar da shugabannin kananan hukumomi na Jigawa.

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce kiraye-kirayen da ake yi a kan tsige shugaban kasa Muhammadu Buhari daga mulki bai dace ba kuma ba zai samu goyon bayansa ba.

Lamido, wanda ya sanar da hakan ga manema labarai yayin taron rantsar da shugabannin kananan hukumomi 27 da aka zaba a jiharsa, ya ce hakan kira ne kwatankwacin wanda ya dinga yi ga shugaban kasan.

Tsohon gwamnan wanda ya jaddada cewa bashi da wata matsala a tsakaninsa da shugaban kasa, ya kara da cewa yana kalubalansa ne saboda siyasa kuma da iya fadin gaskiyarsa.

Tsohon gwamnan, wanda ya yi magana a kan lamurran kasar nan daban-daban, ya tabbatar da cewa har yanzu lokacin cikar burinsa bai yi ba.

Ya kara da cewa abinda jam’iyyar PDP take bukata a halin yanzu shine daidaituwa da kuma hadin kai baki daya, jaridar Daily Trust ta wallafa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here