ISWAP: Gwamnatin Najeriya ta Tabbatar da Mutuwar shugaban Kungiyar, Al-Barnawi
Rundunar sojan Najeriya ta tabbatar da mutuwar Abu Musab al-Barnawi, wanda shi ne shugban ƙungiyar IS na Yammacin Afirka wadda aka fi sani da ISWAP.
“Ya mutu kuma zai ci gaba da kasancewa matacce,” a cewar Hafsan Hafsoshin Tsaro Janar Lucky Irabor.
Sai dai Janar Irabor bai bayar da wani ƙarin bayani ba game da mutuwar Barnawi, wadda aka fara ruwaitowa a watan Satumba.
Ƙungiyar ta ISWAP ba ta ce komai ba game da lamarin, wadda ake yi wa kallon ƙungiyar masu iƙirarin jihadi mafi ƙarfi a Najeriya tun bayan mutuwar shugaban Boko Haram Abubakar Shekau a farkon wannan shekarar.
Bayan haka ne kuma mayaƙan Boko Haram ɗin suka dinga miƙa wuya ga ISWAP da kuma sojojin Najeriya.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here