Hujjar da yasa na Saka wa Tagwayena Sunan Buhari da Al-Makure – Gwamnan Nasarawa
Gwamnan jihar Nasarawa ya rada wa tagwayensa sunan shugaba Muhammadu Buhari da na Umar Al-Makura.
Ya ce ya rada wa yaransa sunayensu ne saboda darajawa da mutuntawa da ke tsakaninsa da shugabannin biyu.
Manyan masu fadi a ji, kamar mataimakin gwamnan jihar, kakakin majalisar jihar da sauransu sun halarci taron.
Read Also:
Gwamnan jihar Nasarawa ya rada wa tagwayensa sunan Shugaba Muhammadu Buhari da na Sanata Umar Tanko Al-Makura, jaridar Daily Trust ta wallafa.
Bayan amaryar gwamnan, Hajiya Farida Abdullahi Sule, ta haifi zankada-zankadan tagwayenta, an yi shagalin sunan a ranar Talata a cikin fadar sarkin Gudu a karamar hukumar Akwanga, Alhaji Sule Bawa, wanda shine mahaifin gwamnan.
Gwamnan ya ce: “Na radawa yarana sunayen shugaba Muhammadu Buhari da na Sanata Umar Tanko Al-Makura saboda girmamawa ta a garesu.