An Tsinci Gawar ‘Yan Ci-rani 15 a ƙasar Tunisia

 

Dakarun tabbatar da tsaro na gaɓar teku a ƙasar Tunisia sun ce sun tsinci gawa 15 waɗanda ruwa ya hakaɗo zuwa gaɓar ruwan birnin Mahdia.

Jami’an suka ce gawarwakin sun zugwanye, wani abu da ke nuna cewar sun daɗe a cikin teku.

Yanzu haka hukumomin na cewa suna ci gaba da ƙoƙarin tantance su, sai dai sun tabbatar da cewa mutanen sun fito ne daga ƙasashen Afirka.

Dubban matasa daga Afirka ne kan yi yunƙurin tsallake tekun Mediterranean a ƙoƙarinsu na tsallakawa Turai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here