Shugaba Tinubu na Shirya Yiwa Majalisar Ministoci Garambawul

 

FCT, Abuja – Akwai yiwuwar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yiwa majalisar ministocinsa garambawul.

Idan ba wani sauyi aka samu ba, Shugaba Tinubu zai yi garambawul ɗin ne a cikin sati mai zuwa.

Jaridar Tribune ta rahoto cewa wata majiya mai tushe a fadar shugaban ƙasa ta ce garambawul ɗin za a yi shi ne domin a kawo sababbin fuskokin da za su ƙara ɗaga darajar gwamnati.

Yaushe Tinubu zai yi garambawul?

Majiyar ta bayyana cewa akwai yiwuwar Tinubu ya yi garambawul ɗin kafin ya tafin taron majalisar ɗinkin duniya (UNGA) wanda za a yi a birnin New York a cikin sati mai zuwa.

Majiyar ta ce Shugaba Tinubu yana sane da ƙorafe-ƙorafen da ake yi na rashin kataɓus ɗin wasu ministocinsa kuma a shirya yake ya sallame su.

Majalisar ta ƙara da cewa an kammala haɗa jerin sunayen ministocin da za a kora daga gwamnatin.

“Shugaba Tinubu bai gamsu da kataɓus ɗin wasu daga cikin ministocinsa ba kuma a shirye yake ya sallame su.”

“Bayan ya dawo daga taron UNGA, shugaban ƙasa zai kafa sabuwar majalisar ministoci.”

– Wata majiya

Jaridar ta ƙara da cewa wani tsohon minista a gwamnatin Muhammadu Buhari na daga cikin waɗanda ake sa ran ba muƙamin minista.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here