An Samu Na’ukan Cutar Polio Guda 70 a Jihohi 14 na Arewacin ƙasar – Gwamnatin Najeriya

 

Najeriya na fuskantar ƙaruwar yaɗuwar sabuwar na’uin cutar polio ta cVPV2, kamar yadda Hukumar Kiwon Lafiya a Matakin Farko ta bayyana.

Babban daraktan hukumar, Dokta Muyi Aina ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja a wani taro da ya yi da shugabannin addini, wanda hukumar ta shirya tare da haɗin gwiwar Gidaunar Sultan wato Sultan Foundation for Peace and Development.

Ya ce an samu jimillar na’uin 2 cVPV2 guda 70 a ƙananan hukumomi 46 a jihohi 14 na arewacin Najeriya.

A cewarsa, “wannan na nuna cutar na cigaba da yaɗuwa saboda ƙarancin aiwatar da allurar riga-kafi. Dole a canja wannan tsarin. Dole mu tabbatar kowace mace ta samu kula a lokacin da take ɗauke da juna biyu, sannan ya zama ƙwararru ne suke amsar haihuwa, sannan mu tabbatar kowane jariri na kammala allulorinsa na riga-kafi kamar yadda aka tsara.”

Ya yi kira ga shugabannin addini da su ƙara ƙaimi domin tabbatar da shirin allurar riga-kafi na tafiya daidai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here