Tallafin Corona: Majalisar Dattawa ta Bada Umarnin  Kamo Mata Shugaban NDDC

 

Majalisar dattawa ta bada umarnin kwamushe shugaban NDDC da laifin salwantar da kudi.

Majalisar a baya ta umarci ya zo ya bada bayanin yadda ya salwantar da kudaden amma ya ki.

A halin yanzu Sufeto-janar na ‘yan sanda ne zai kamo shi ya kawo shi gaban majalisar a watan gobe.

Kwamitin majalisar dattijai kan da’a, gata da kuma koke-koken jama’a, ya bayar da sammacin kame kan mai rikon kwarya na Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC), Effiong Okon Akwa, saboda kin mutunta gayyatar kwamitin.

Kwamitin, a lokuta daban-daban, ya gayyaci shugaban NDDC da ya ba da bayani kan Naira biliyan 6.2 da aka kashe na kwamitin tallafin COVID-19, Daily Trust ta ruwaito.

Jin haushin rashin zuwan shugaban NDDC din a zaman da ta yi a ranar Litinin, Kwamitin, karkashin jagorancin Sanata Ayo Akinyelure (PDP Ondo ta Tsakiya), sun yanke shawara cewa Majalisar Dattawa za ta tuntubi Sufeto-Janar na ’Yan sanda ya kamo shi.

Za a baiwa Sufeto-janar ya kamo hugaban NNDC ya kawo shi gaban kwamitin ba tare da saurarawa ba a ranar 9 ga watan gobe.

“Bayan ya gayyaci shugaban hukumar ta NDDC har sau hudu ba tare da girmama gayyatar ba, wannan kwamitin ba shi da wani zabi da ya wuce kiran sashin kundin tsarin mulki da abin ya shafa don sammacin kama duk wanda ya kasance shugaban hukumar a yanzu.

“Takardar karar da wani jami’in yada labarai ya shigar kan hukumar kan zargin barnatar da N6.2bn na tallafin COVID-19 a shekarar da ta gabata yana da girma kuma yana da nauyi a yi watsi da shi.

“Don cimma wannan, tsarin da tsarin mulkin da ake bukata na wannan kwamitin za su bi wajen tabbatar da cewa Sufeto Janar na ‘yan sanda ya gabatar da shugaban NDDC a gabanta a ranar 9 ga Maris, 2021 lokacin da zama na gaba zai gudana.”

NDDC, a karkashin korarren Farfesa Daniel Pondei karkashin jagorancin kwamitin rikon kwarya (IMC), ta yi ikirarin kashe N6.25bn na tallafin COVID-19 a shekarar 2020 a tsakanin jahohin tara mai. Amma Shugaban Kwamitin Rarrabawa na COVID-19 na hukumar, Ambasada Sobomabo Jackrich, a cikin wata takardar koke da aka aika wa kwamitin, ya ce ba a kashe ko sisin kwabo ba don wannan dalili ta IMC na Hukumar a lokacin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here