Aliyu Magatakarda Wamakko ya Lashe Zaɓen Sanatan Sokoto ta Arewa

 

Tsohon gwamnan Sokoto, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya lashe zaɓen sanatan Sokoto ta Arewa, a zaɓen cike giɓi da aka gudanar jiya a wasu sassa na Najeriya.

Magatakarda ya samu nasara ne a kan mataimakin gwamnan Sokoto Mannir Muhammad Ɗan’iya.

Wamakko ya samu ƙuri’a 141,468 yayin da babban abokin takararsa Ɗan’iya ya samu 118,445 a zaɓen, wato bambancin ƙuri’a 23,023 tsakaninsu.

A baya dai, an bayyana zaɓen a matsayin wanda bai cika ba saboda zarge-zargen maguɗi da tashe-tashen hankula da amfani da ‘yan banga wajen tarwatsa zaɓe.

Wamakko ya yi gwamnan jihar Sokoto sau biyu, kuma a 2015 ya ci kujerar sanata ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Yanzu dai ana jiran sakamakon kujerar sanata daga shiyya biyu ta ɗan majalisar dattijai daga jihar Sokoto da suka rage.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here