Sabon Ministan Birnin Tarayya, Wike ya yi Barazanar Rusa Gidaje

 

Sabon ministan babban birnin tarayyar Najeriya – Abuja, Nyesom Wike, ya yi barazanar fara rusa gidajen da aka gina ba bisa ka’ida ba.

Wike ya bayyana haka ne a jawabinsa na farko bayan rantsar da shi domin soma aiki.

“Idan kun gina gidajenku a wuraren da aka saba ka’ida, sai an rusa su,” in ji Wike.

Tsohon gwamnan Ribas din yana cikin ministoci 45 da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da su a fadarsa da ke Abuja.

Wike ya sha alwashin yin tir da tsarin da ke kawo cikas ga taswirar babban birnin tarayyar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com