Sabbin Wuraren da za mu kai wa hari a Iran da Lebanon – Isra’ila
Ministan tsaron Isra’ila, Isreal Katz ya ce shi da babban hafsan hafsoshin rundunar IDF, janar Eyal Zamir sun amince da sabbin wuraren da za a kai hare-hare a Iran da Lebanon.
Read Also:
Hakan dai na zuwa ne kwana guda bayan da Isra’ila ta ce tana shirin mamaye yankunan kudancin Lebanon har zuwa kogin Litani, har zuwa lokacin da za a kawar da barazanar Ƙungiyar Hizbullah da ke samun goyon bayan Iran.
Kafofin yada labaran Labanon sun ruwaito hare-hare ta sama da Isra’ila ta kai a wurare daban-daban a jiya Laraba ciki har da birnin Tyre.
Isra’ila ta ce kimanin rokoki goma Ƙungiyar Hezbullah ta harba a birnin Haifa da ke arewacin kasar.
Ta ce an kakkabo wasu daga cikinsu, yayin da wasu kuma aka bari suka faɗa wasu filaye.






