Sabbin Wuraren da za mu kai wa hari a Iran da Lebanon – Isra’ila

 

Ministan tsaron Isra’ila, Isreal Katz ya ce shi da babban hafsan hafsoshin rundunar IDF, janar Eyal Zamir sun amince da sabbin wuraren da za a kai hare-hare a Iran da Lebanon.

Hakan dai na zuwa ne kwana guda bayan da Isra’ila ta ce tana shirin mamaye yankunan kudancin Lebanon har zuwa kogin Litani, har zuwa lokacin da za a kawar da barazanar Ƙungiyar Hizbullah da ke samun goyon bayan Iran.

Kafofin yada labaran Labanon sun ruwaito hare-hare ta sama da Isra’ila ta kai a wurare daban-daban a jiya Laraba ciki har da birnin Tyre.

Isra’ila ta ce kimanin rokoki goma Ƙungiyar Hezbullah ta harba a birnin Haifa da ke arewacin kasar.

Ta ce an kakkabo wasu daga cikinsu, yayin da wasu kuma aka bari suka faɗa wasu filaye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here