Rahotannin da Ake Yadawa a Kafafen Yada Labarai na Cewa PDP ta Zabi Wike Kawai Jita-Jita ne – Debo Ologunagba

 

A dai dai lokacin da ‘yan Najeriya ke jiran a bayyana gwamnan Rivers, Nyesom Wike a matsayin mataimakin Atiku Abubakar, jam’iyyar PDP ta fasa kwai.

A wani sako daga jam’iyyar a ranar Laraba, 15 ga watan Yuni, sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa, Debo ya bayyana cewa ba a zabi Wike ba.

Ologunagba, ya ce ikirarin cewa an riga an zabi Wike a ga tafiyar karya ne domin har yanzu dai ana ta shawari a kai.

Abuja – Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta yi watsi da rade-radin da ake yi cewa kwamitinta ya zabi gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike ya zama dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar.

Vanguard ta ruwaito cewa, kwamitin zaben na jam’iyyar PDP, ya yi taro a jiya, domin cika aikin da ya rataya a wuyansa na ba da shawarar kan abokin tafiyar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Alhaji Atiku Abubakar.

Da yake magana kan wannan lamari a Abuja, Laraba, Sakataren Yada Labarai na kasa na PDP, Debo Ologunagba, ya ce rahotannin da ake yadawa a kafafen yada labarai na cewa PDP ta zabi Wike kawai jita-jita ne.

Ya ce a halin yanzu kwamitin ayyuka na kasa na jam’iyyar na duba lamarin tare da tuntubar juna, domin duba wanda ya fi kowa cancanta ya yi takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar a zaben 2023.

A halin da ake ciki, Ologunagba, wanda ya jaddada cewa PDP ta fara gudanar da ayyukanta na tantancewa, ya sanar da cewa za a yi taro a yau Laraba da karfe 11 na safe, inda ya ce ana sa ran za a duba kwamitin da ke shawari kan lamarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here