Ƴan Bindiga sun yi Awon Gaba da Gomman Fasinjoji a Habasha

 

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da gomman fasinjoji da suka taso daga Addis Ababa, a yankin Oromia da ke ƙasar Habasha.

Lamarin ya auku ne a Ali Doro, kusa da inda aka sace ɗaliban jami’a kusan 100 a lokacin da suke hanyar komawa ɗakunan kwanansu a watan Yulin bara.

Waɗanda suka tsira da hukumomin yankin sun ɗaura alhakin sace fasinjojin a kan ƙungiyar Oromo wato OLA, wadda ta ƴantawaye ce da suke da ƙarfi a yankin.

Sai dai ƙungiyar ta fito ta musanta zargin, inda ta ce ba ta da hannu a lamarin.

Ta ce ita ma ta samu labari, amma “za ta gudanar da bincike.”

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton gwamnatin ƙasar ba ta ce komai ba.

Garkuwa da mutane – ciki har da fasinjoji – ya fara zama ruwan dare a yankin, inda suke sace mutane domin karɓar kuɗin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here