‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Mutane 3 Tare da Yaran Ma’aikacin Gwamnatin Tarayya 2

 

Wasu bata gari da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun kai hari Unguwar Chukuku da ke Abuja.

Mutanen dauke da bindigu sun kutsa gidan wani ma’aikacin hukumar gwamnatin tarayya sun sace yaransa biyu.

Har wa yau, sun kuma shiga wani gidan inda suka sace ma’aikaciyar jinya a asibiti da wasu mutanen biyu.

FCT, Abuja – Wasu da ake zargi masu garkuwa da mutane ne sun kai hari unguwar Chukuku da ke karamar hukumar Kuje na babban birnin tarayya Abuja daga daren ranar Lahadi zuwa asubahin Litinin.

Daily Trust ta rawaito cewa maharan sun sace mutane biyar, cikin mazauna unguwar da suka kutsa domin kai hari.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigan sun rika barin wuta a yayin da suke kutsawa cikin unguwar domin su firgita mutane.

Wani mazaunin wanda ya nemi a boye sunansa ya ce ‘yan bindigan sun tafi gidan wani ma’aikaci a hukumar gwamnatin tarayya suka sace yaransa biyu, Daily Trust ta rawaito.

Mazauna unguwar sun kuma ce ‘yan bindigan sun tafi wasu gidajen inda suka sace wata ma’aikaciyar jinya da wasu mutane biyu.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Adeh Josephine ta ce bata da masaniya kan afkuwar lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here