Yanda ‘Yan Bindiga Suka Salwanta Rayukan Jama’a

Masu garkuwa da mutane suna cigaba da kai hare-hare kauyakun jihar Kaduna.

‘Yan ta’addan sun kai hari Kajuru, Igabi, Giwa da Zangon Kataf ranar Litinin da Talata.

Sakamakon hare-haren, mutane 16 sun rasa rayukansu, sun kuma yi garkuwa da wasu.

‘Yan bindiga sun cigaba da kai hare-hare kananun hukumomi da ke karkashin jihar Kaduna, kamar Kajuru, Igabi, Giwa da Zangon Kataf, inda suka kashe a kalla mutane 16 a ranar Litinin da Talata.

Sun saci mutane da dama, kuma sun harbi a kalla mutane 4.

Sun kai hari a ranar Lahadi hanyar Kaduna zuwa Abuja har suka yi sanadiyyar mutuwar mutane 15, kuma suka kwashe daliban jami’ar Ahmadu Bello 8.

Gwamnatin jihar Kaduna, ta tabbatar da kisan mutane 11 a kauyen Albasu, da ke karkashin karamar hukumar Igabi, Daily trust ta ruwaito.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan, ya ce wasu mutane 4 sun rasa rayukansu sakamakon raunukan da ‘yan ta’addan su ka ji musu.

Jami’an tsaro sun ce an kashe wani Albarka Addu’a, tsohon dagacin kauyen Kyemara Gari a ranar Lahadi, bayan ‘yan bindigan sun yi garkuwa da wasu mutane 2 a Maraban Kajuru a karamar hukumar Kajuru.

Ya kuma tabbatar da harin da aka kai kauyakun Fatika, Kaya da Yakawada da ke karkashin karamar hukumar Giwa a ranar Talata, wanda hakan yayi sanadiyyar mutuwar mutane 2, sannan an yi garkuwa da mutane da dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here