Yankuna da Jahohin da Suka fi Samun Wakilai a Nade-Naden Shugaba Buhari

 

Biyo bayan zargin da Bishop Mathew Kukah yayi wa Shugaban kasa Muhaammadu Buhari na son kai, an koma ga tattauna wasu yankuna ne suka fi samun wakilai a nade-naden Shugaban kasar.

Wannan zauren ya kawo bayani dalla-dalla kan nade-nade 190 da Buhari yayi a kwanaki kamar yadda jaridun Premium Times da Daily Trust suka ruwaito.

Jaridun biyu sun yi nuni ga wata takarda daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya.

Rabe-raben yanki-yanki

1. Kudu maso yamma – Nade-nade 64

2. Arewa maso yamma – Nade-nade 37

3. Arewa maso gabas – Nade-nade 29

4. Kudu maso kudu – Nade-nade 24

5. Arewa maso tsakiya – Nade-nade 21

6. Kudu maso gabas – Nade-nade 15

A matakin jaha, jahar Ogun ce ke da mukaman siyasa mafi yawa da Shugaban kasa Buhari nada tun bayan sake zabensa a 2019 inda take da 17 cikin nade-nade 190 a daidai lokacin wannan rahoton. Kalli rabe-rabensu a kasa.

Rabe-raben Jiha-jiha: Guda biyar da ke kan gaba

1. Jahar Ogun – 17

2. Jahar Adamawa – 14

3. Jahar Kano – 12

4. Jahar Lagos – 12

Dalla-dalla: Kudu da Arewa

1. Yankin kudu (jahohi 17) – Nade-nade 103

2. Yankin Arewa (jihohi 19) – Nade-nade 87

Legit.ng ta tattaro cewa dukkanin nade-naden na aiki a ofishoshin Shugaban kasa, mataimakin Shugaban kasa, uwargidar Shugaban kasa da uwargidar mataimakin Shugaban kasa.

Premium Times ta nusar cewa dakatar ofishin sakataren gwamnatin bai sanya nade-naden da Shugaban kasar yayi a ma’aikatun tarayya (sakatarorin dindindin), hukumomi da masana’antu ba.

Hakazalika ba ya dauke da nade-naden jakadu da na hukumomin tsaron kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here