Kashi 5% na ƙananan Yara na Fama da Tarin Fuka a Jihar Kano – Masana

 

Masana sun koka kan yadda cutar tarin fuka ta yawaita cikin ƙananan yara a jihar Kano da ke Arewacin Najeriya.

Jihar Kano – Kungiyar kula da lafiya ta SFH ta yi taro na musamman kan ciwon tarin fuka a jihar Kano.

Masana lafiya sun tattauna kan yadda tarin fuka ya yawaita tsakanin yara ƙanana a fadin jihar Kano.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kungiyar SFH ta bayyana kalubalen da ake fuskanta a jihar kan cutar.

Yawaitar tarin fuka tsakanin yara a Kano

Kungiyar ta bayyana cewa ana samun yaɗuwar cutar tarin fuka a tsakanin yara ƙanana da kashi 5%.

Hakan na nuni da cewa duk cikin yara ƙanana 100 a jihar ana samun yara biyar da ke dauke da cutar.

Wani ma’aikacin jinya, Dakta Ibrahim Umar ya bayyana cewa jihar Kano ce gaba gaba wajen samun masu tarin fuka a Najeriya.

Kalubalen tarin fuka a jihar Kano

Wata ma’aikaciyar lafiya mai suna, Jane Adizue ta bayyana cewa ana fuskantar kalubale da dama dangane da tarin fuka a Kano.

Jane Adizue ta ce akwai kalubalen rashin gwaji da wuri, rashin samun kulawa da rashin bayyana yadda mai cutar ya kamata ya rayu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here