Yadda Zanga-Zanga ta Kasance a Babban Birnin Tarayya

 

Yan sanda sun harba hayaki mai sa hawaye kan masu zanga-zanga domin tarwatsa su a Abuja, Babban birnin Najeriya.

Masu zanga-zanga an Abuja, babban birnin Najeriya sun mamaye titunan birnin suna bayyana takaicinsu ga tabarbarewar al’amura da matsalar yunwa a kasar.

Wata kotu a hukuncin da ta yanke ranar Laraba da daddare ta umarci masu zanga-zangar da su yi gangaminsu a filin wasa na kasa da ke wajen babban birnin a maimakon mamaye dandalin Eagle Square da ke tsakiyar birnin.

Sai dai bayan da suka yi dandazo a kofar shiga filin wasan ne masu zanga-zangar suka fasa shiga filin Hasan inda suka bar harabar wajen suka nufi cikin gari.

Zuwa yanzu babu cunkoson ababen hawa a birnin saboda wuraren kasuwanci har da bankuna na rufe. An jibge jami’an tsaro a muhimman wurare a Abuja.

Ana fargabar zanga-zangar na iya rikidewa zuwa tashin hankali saboda burus da umarnin kotu.

Wasu masu zanga-zangar da suka yi magana da BBC sun ce suna gudanar da zanga-zanga kamar yadda doka ta basu dama.

“Babban muradinmu shi ne a maido da tallafin mai. Ya kamata gwamnati ta janye da matakin da ta dauka,” in ji Abiodun Sanusi.

Suna kuma so gwmanati ta yi gagarumin garambawul a tsarin zaben kasar da bangaren shari’a.

“Abin da muke so shi ne kasar nan ta koma tsarin majalisa daya. A seke majalisar dattijai, a kyale majalisar wakilai,” Abiodiun ya bayyana.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here