Shugaba Muhammadu Buhari ya Shiga Ganawa da Shugaban Hukumar INEC

Shugaba Buhari ya gana da shugaban hukumar INEC biyo bayan hare-hare da ake kai wa ofisoshin hukumar.

A tare da shugaban na INEC akwai kwamishinoni biyar da aka yi tattaunawar dasu a Abuja.

Ana sa ran sun tattauana mafita ne kan karuwar hare-hare da ake kai wa ofishoshin INEC a fadin kasar.

Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Talata ya gana da Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, Channels Tv ta ruwaito.

Farfesa Yakubu ya kasance tare da kwamishinonin INEC guda biyar a taron, wanda aka yi a dakin taro na Uwargidan Shugaban Kasa a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.

Taron na iya zama mai nasaba da hare-haren da aka kai kan cibiyoyin INEC na baya-bayan nan a duk fadin kasar.

Rahoton Premium Times ya ruwaito shugabn na INEC a ranar 27 ga Mayu, yana cewa an kai wa ofisoshi da wuraren aikinta hari sau 41 a cikin shekaru biyu da suka gabata.

Sai dai, a cikin makonni hudun da suka gabata, ofisoshin hukumar guda 11 ko dai an cinna musu wuta ko an lalata su, a cewar shugaban na INEC.

A ranar Litinin, hukumar zaben ta sha alwashin gudanar da zaben gwamnan Anambra, wanda aka shirya za a yi a ranar 6 ga Nuwamba, duk da karuwar matakan rashin tsaro a fadin kasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here