Dakarun Fadar Shugaban Kasa Sun Damke Manyan ‘Yan Ta’adda 8

 

Hedkwatar Tsaro ta Najeriya tace dakarun sojoji sun damke manyan ‘yan ta’adda 8 a babban birnin tarayya na Abuja.

Gagarumin aikin kamar yadda shugaban rundunar ya bayyana, dogaran fadar shugaban kasa ne suka yi shi a Deidei Abbatoir da kauyen Dukpa daka Gwagwalada.

An yi wannan aiki ne kasa da watanni biyu bayan sojojin fadar shugaban kasa 8 sun halaka a wani farmaki da ‘yan ta’adda suka kai musu.

FCT, Abuja – Rundunar sojin Najeriya ta kai samame maboyar ‘yan ta’adda inda suka cafke manyan ‘yan ta’adda takwas a yankin.

Hedkwatar tsaro ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis, 25 ga watan Augustan 2022 inda ta kara da cewa an kama ‘yan ta’addan ne a maboyarsu dake Deidei Abbatoir da kauyen Dukpa a karamar hukumar Gwagwalada, The Nation ta rahoto.

Dakarun fadar shugaban kasan ne suka aiwatar da aikin. Idan za a tuna, hafsoshin soji biyu da sojoji shida daga cikin dogaran fadar shugaban kasan sun rasa rayukansu sakamakon harin kwanton bauna da ‘yan ta’adda suka kai yankin Bwari.

An gano cewa a sansanin ne ‘yan Boko Haram da mambobin ISWAP ke kafa dandalinsu.

Kamar yadda daraktan yada labarai na rundunar, Manjo Janar Musa Danmadami ya bayyana, an kai samamen a ranar 13 ga watan Augusta.

“A samamen, mutum takwas aka kama da zargin ta’addanci, bindigu kirar AK47 guda biyar da wasu guda uku aka samu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here