Dakaru 105 ne Suka Rasa Rayukansu a Yakin da Ake yi a Kan Iyakar Azerbaijan –
Armeniya

 

Firaministan Armeniya Nikol Pashinyan ya ce fiye da sojojin kasar 100 ne aka kashe a rigingimun kan iyaka da Azerbaijan da ya barke tun ranar Litinin.

A nata bangaren kasar Azerbaijan ta ce dakarunta 50 ne suka rasa rayukansa a sanadiyyar rikicin da kasashen biyu ke dora alhakinsa a kan juna.

Yayin da yake jawabi ga majalisar dokokin kasar Mista Nikol Pashinyan ya ce dakarun kasar 105 ne suka rasa rayukansu tun ranar Litinin da daddare a wasu hare-hare da dora alhakinsu kan kasar Azerbaijan.

Tuni dai kasashen Rasha da Amurka suka yi kira ga kasashen biyu da su tsagaita wuta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here