Everton ta Doke Arsenal 1-0

 

Sabon kocin Everton Sean Dyche ya fara wasa da ƙafar dama bayan da ya samun nasarar doke Arsenal da ci 1-0.

A ranar Litinin ne aka naɗa Dyche bayan tafiyar Frank Lampard, wanda aka kora yayin da ƙungiyar ke ƙasar teburin Premier.

Ƙungiyar ta samu nasararta ta farko cikin wasa 11 da ta buga a duka gasannin Ingila.

Ɗan wasan tsakiya James Tarkowski ne ya zura ƙwallo ɗaya ta ka, da ta bai wa ƙungiyar nasara a kan Arsenal wadda ke mataki na ɗaya a teburin.

Da wannan sakamako, tazarar da ke tsakanin Arsenal da Manchester City ta biyu zai ragu zuwa maki biyu idan Cityn ta yi nasara a kan Tottenham ranar lahadi.

A gefe guda kuma, ‘yan Najeriya na ci gaba da kokawa kan ƙarancin kuɗin, inda suke shafe awanni a kan dogayen layuka don cirar su a na’urorin ATM.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here