Faransa ta yi Allah wadai da Goyan Bayan Sanya Hijabi  a Turai

 

Gwamnatin Faransa ta yi Allah wadai da wani kamfen da ɓangaren kare haƙƙin ɗan Adam na majalisar Turai ta ƙaddamar a intanet da nufin ƙarfafa amincewa da tsarin sanya hijabi ga mata a Musulunci.

Matakin wanda ya samu goyon bayan ƙungiyar Tarayyar Turai kuma take ɗaukar nauyi – yanzu an janye shi.

Shirin ya ƙunshi fuskokin mata, wasu sanye da mayafi ko hijabi wasu kuma babu.

Taken shirin shi ne: “Ado yana cikin bambance-bambance kamar yadda sanya hijabi ƴanci ne; ya kamata a girmama hijabi.”

Majalisar Turai mai hedikwata a Strasbourg ta ce matakin na cikin shirinta na yaƙi da kyamar musulmi.

Amma a Faransa, ɓangarorin siyasa ne suka mayar da martani.

Ministar matasa a gwamnatin shugaba Macron, Sarah el-Hairy ta ce shirin wani matakin na ƙarfafa sanya hijabi ya saɓa wa aƙidun Faransa.

Eric Zemmour da ke neman takarar shugaban ƙasa da za a yi watan Afrilu mai zuwa, ya faɗi a Twitter cewa: “Musulunci addini ne da ya saɓawa ƴanci, kuma wannan maƙiyin gaskiya ne.”

Saboda adawa da matakin a Faransa, majalisar Turai ta janye kamfen ɗin tana mai cewa za ta bi wasu hanyoyi na isar da saƙon.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here