Za’a Sake Fasalin Tsarin Biyan Haraji na Kasa da Kasa

An bada sanarwar sa ke fasalin tsarin biyan haraji na kasa da kasa wanda shi ne mafi girma bayan watanni ana tattaunawa tsakanin kasashe 140.

An kamala Tattaunawar da aka yi a Paris karkashin jagorancin kungiyar hadin-kan tattalin arziki da ci gaba da matsayar da ta nemi kamfanonin kasashen waje biyan mafi kankanta haraji na kashi goma sha biyar.

A shekarar 2023 matsayar da aka cimma za ta soma aiki.

Wakilin BBC ya ce kwararu daga kungiyar ta OECD sun yi ammanar cewa kasashe za su samun karin kudin da yawansu ya kai dala biliyan 150 daga harajin da za a karba a kowace shekara a duniya.

Sai dai kasashe hudu da suka hada da Kenya da Najeriya da Sri lanka da kuma Pakistan kawo yanzu ba su shiga cikin yarjejeniyar ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here