Gwamnatin Jahar Kano ta Zabtare Albashin Ma’aikata

 

Gwamnatin jahar Kano ta sanar da daina biyan ma’aikatanta karancin albashin N30,000.

Jihar ta gaggauta komawa biyan karancin albashin zuwa N18,000 a ranar 6 ga watan Janairu.

Gwamnatin ta bayyana cewa hakan ya biyo bayan karayar tattalin arzikin da aka shiga saboda Covid-19.

Annobar korona ta yi mummunar illa ga tattalin arzikin jihohi da dama na Najeriya ballantana jihar Kano.

Hakan yasa gwamnatin jihar Kano ta sanar da komawa biyan ma’aikatanta karancin albashin N18,000 a maimakon N30,000 da ta fara bayan boren da kungiyar kwadago tayi, The Cable ta ruwaito.

A yayin tabbatar da wannan cigaban, mai magana da yawun Gwamna Umaru Ganduje, Salihu Tanko-Yakasai, ya ce halin da kasar nan ta shiga sakamakon annobar korona ce ta saka hakan.

Ya ce: “Gwamnatin jihar ta koma biyan tsohon karancin albashi saboda halin da ta shiga. Abinda muke samu a matsayin gwamnati yanzu ya ragu kuma ba za mu iya cigaba da biyan N30,000 ba a matsayin karancin albashin.”

Amma kuma, ma’aikatan gwamnatin da ke jihar sun jajanta yadda gwamnatin jihar bata bada wata sanarwa ba kafin ta fara zabtare musu albashi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here