Hezbollah ta kai Hare-hare Fiye da 60 kan Isra’ila

 

Ƙungiyar Hezbollah ta ƙasar Lebanon ta ce ta kai hare-hare guda 63 kan Isra’ila a ranar Lahadi.

A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Telegram, Hezbollah ta bayyana cewa ta yi amfani da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, da kuma harbin manyan bindigogi wajen kai hare-haren kan sojojin Isra’ila, a cikin Isra’ila da kuma kudancin Lebanon.

Dangane da barazanar da Hezbollah ke yi, Isra’ila ta ƙaddamar da farmakin ƙasa a kudancin Lebanon.

Tun daga ranar 1 ga watan Maris, hare-haren Isra’ila a Lebanon sun yi sanadin mutuwar mutane 1,029, tare da jikkata 2,786, yayin da sama da mutum miliyan guda suka rasa matsugunansu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here