Harin Iran ya Haddasa Gobara a Matatar Man Haifa da ke Isra’ila

 

Wani sabon harin makami mai linzami da Iran ta kai ya haddasa gobara a wata matatar mai da ke Haifa a arewacin Isra’ila.

Bidiyoyin da aka fitar sun nuna yadda wuta ta kama ɗaya daga cikin manyan tankunan matatar, inda kuma hayaƙi ya rika tashi sama.

Kamfanin dillancin labarai na AP ya ruwaito cewa wannan ne karo na biyu da Iran ke kai hari kan matatar mai ta Haifa a yayin wannan rikici na baya-bayan nan.

Rahotanni sun ce an samu nasarar shawo kan gobarar.

Hukumar kashe gobara ta Isra’ila ta shaida wa Reuters cewa wani tankin ajiyar mai ya samu illa sakamakon harin.

Isra’ila da na da matatun mai guda biyu ne.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here