Jawabin Gwamnan Kano Gabannin Zanga-Zanga 

 

Jihar Kano – Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya ce gwamnati ba za ta lamunci wani yunkuri ba zai kawo tashin hankali ba a zanga-zangar da za a yi gobe Alhamis.

Abba Kabir ya faɗi haka ne a lokacin da yake jawabi ga ’yan kasuwa, sarakunan gargajiya, da malaman addini a gidan gwamnati da ke Kano yau Laraba.

Gwamna ya jaddada cewa zanga-zanga ba za ta kai mutane ko’in ba, bisahaƙa ya ja kunnen matasa su guje wa tada zaune tsaye, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

Gwamnan Abba ya gayyaci masu zanga-zanga

“Mun samu sahihan bayanan sirri cewa wasu daiɗaikun mutane sun ɗauko hayar ƴan daba domin tada fitina a jihar Kano. Ina tabbatar muku da cewa gwamnati ba za ta lamunci haka ba.

“A maimakon haka, ina mika goron gayyata ga masu son gudanar da zanga-zanga da su zo gidan gwamnati, inda zan ji dadin sauraren koke-kokensu, sannan mu tattauna da su.”

– Abba Kabir Yusuf.

Gwamna ya ambaci wasu tsare-tsaren da gwamnatinsa ta kawo na inganta rayuwar al’umma da kuma tsamo su daga halin wahalar da ake ciki.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here